Hausa News

Lauyoyin Mawaƙi Rarara sun bayyana a gaban Kotu

Add

Lauyoyin Mawaƙi Rarara sun bayyana a gaban Kotu

Lauyoyin Mawaƙi Dauda Kahutu Rarara sun bayyana a Kotun Shari’ar Muslunci da ke Rijiyar Zaki a Kano.

Idan zaku iya tunawa wani ɗan kasuwa ne ya yi ƙararar mawaƙin bisa cewa yana binsa bashi kuɗi kimanin Miliyan Goma na wayoyi da yake karɓa yana rabawa mutane.

A zaman Kotun da ya gabata dai Kotun ta bayyana yadda mawaƙin ko lauyoyinsa suka gaza amsa sammacinta.

To amma a Alhamis ɗin nan lauyoyinsa sun bayyana ƙarƙashin Barrister G.A Badawi inda ya nemi a basu damu su yi nazarin tuhume-tuhumen da ake yiwa mawaƙin, domin su yi martani.

Kotun ta sanya ranar Litinin 17 ga watan Afrilun da muke ciki domin ci gaba da wannan shari’ar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button